IQNA

Cibiyar Harkokin Musulunci Ta Kasar Gyrgystan Ta Samu Karbuwa

17:00 - May 06, 2009
Lambar Labari: 1775019
Bangaren kur'ani: Cibiyar kula da harkokin musulunci da kuma kur'ani da aka bude a cikin 'yan kwanakin a birnin Beshkik fadar mulkin kasar Gyrgystan, ta samu karbuwa a wajen matasan kasar.
Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga mahiyoyin yada labarai na kasar Gyrgustan cewa; Cibiyar kula da harkokin musulunci da kuma kur'ani da aka bude a cikin 'yan kwanakin a birnin Beshkik fadar mulkin kasar, ta samu karbuwa a wajen matasan kasar. Shugaban cibiyar Mahmud Kashgari ya bayyana cewa wannan shi ne karo na farko da aka bude wata babbar cibiyar addinin musulunci a duk fadin kasar, kuma al'ummar kasar musamman ma matasa daga cikinsu sun nuna matukar sha'awarsu da ayyukan da cibiyar yanzu haka ta fara gudanarwa, da hakan ya hada da shirya taruka na addinin musulunci, tare da wayar da kan matasa dangane da muhimmancin da ke tattare da yin koyi da tarbiyar musulunci.

400083




captcha