Bangaren kasa da kasa: Babbar cibiyar bayar da agajin nan ta kasar Qatar ta kalubalanci gwamnatin Isla'ila kan ci gaba da yin gine-ginen da take yi a cikin harabar masallacin Qods mai alfarma, kamar yadda cibiyar ta fara gudanar da wasu shirye-shirye na ci gaba yin fito na fito da wannan mummunar manufa ta Isra'ila kan wurare masu tsarki da ke Qods.
Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga jaridar nan ta kasar Qatar Alrayya cewa; Babbar cibiyar bayar da agajin nan ta kasar Qatar ta kalubalanci gwamnatin Isla'ila kan ci gaba da yin gine-ginen da take yi a cikin harabar masallacin Qods mai alfarma, kamar yadda cibiyar ta fara gudanar da wasu shirye-shirye na ci gaba yin fito na fito da wannan mummunar manufa ta Isra'ila kan wurare masu tsarki da ke Qods. Rahoton ya ci gaba da cewa wannan cibiya ta kan ware wasu kudade da suka kimanin dalar Amurka dubu dari domin rabawa ga palastinawa mazauna birnin Qods da suke fuskantar matsaloli na rashi sakamkon mawuyacin halin da aka jefa su ciki.
403972