IQNA

Isra'ila Ta Hana Gudanar Da Taro Kan Masallacin Qods

12:20 - June 01, 2009
Lambar Labari: 1785500
Bangaren kasa da kasa: Haramtacciyar kasar Isra'ila ta dauki tsauraran matakai na hana gudanar da taron kasa da kasa kan masallcin Qods da aka shirya gudanarwa a birnin mai alfarma na tsawon mako guda.
Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga jaridar Sharq al-ausat cewa; Haramtacciyar kasar Isra'ila ta dauki tsauraran matakai na hana gudanar da taron kasa da kasa kan masallcin Qods da aka shirya gudanarwa a birnin mai alfarma na tsawon mako guda. Taron wanda aka fara gudanarwa jiya ya samu halartar marubuta dam asana daga kasashen duniya daban-daban, amma jim kadan bayan fara gudanar da taron jami'an tsaron Haramtacciyar kasar Isra'ila a cikin kayan sarki sun kai farmakia wurin tare da watsa taron a birnin Qods mai alfarma. Taron dai yana da dangantaka ne da zaben birnin Qods da aka yi a matsayin babban birnin al'adun larabawa na shekara ta 2009, da kuma fadakar da al'ummomin duniya halin da birnin yake ciki, da kuma barazanar da yake fuskanta daga yahudawan sahyuniya.

413122
captcha