IQNA

Azhar Ta Bukaci Da Dakar Da Nuna Wani Fim Da Ya Ci Zarafin Musulunci

15:51 - June 02, 2009
Lambar Labari: 1786489
Bangaren kasa da kasa: Kwamitin manayan malaman addinin musulunci na jami'ar Azhar da ke birnin Alkahira n akasar Masar, sun bukaci da a dakatar da nuna wani fim da aka shirya domin tozarta addinin musulunci ta hanyar wulakanta wurare masu tsarki da ke kasar.
Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga jaridar alwatan ta kasar Saudiyya cewa; Kwamitin manayan malaman addinin musulunci na jami'ar Azhar da ke birnin Alkahira n akasar Masar, sun bukaci da a dakatar da nuna wani fim da aka shirya domin tozarta addinin musulunci ta hanyar wulakanta wurare masu tsarki da ke kasar. Kwamitin malaman ya yi wannan kira ne a cikin wata wasika da ya aike wa shugaban kasar ta Masar Husni Mubarak, da a ciki suka bayyana cewa an shirya wannan fim din domin wulakanta wurare masu tsarki da ke kasar, a kan haka ya zama wajibi a gagguta dakatar da wannan fim din, kuma yanzu haka an shirya nuna shi a gidan sinima da ke birnin Iskandariyya na kasar, a kan haka suka kirayi Mubarak da ya dakatar da hakan domin samun zaman lafiya a kasar.

414307



captcha