Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a Iran Ikna ce ta nakalto daga majiyar labarai ta sakatariyar shirya wannan taro cewa wannan taro za a gudanar da shi ne karkashin daukan dawainiyar hakan da ofishin da ke kula yada al'adun Iran a ketare tare da hadin guiwar cibiyar da ke kula da al'adu da ilimin kur'ani da ke birnin Qum gami da jami'ar Almustapha (SWA) Al'alamiya da wasu cibiyoyi da hukumomi na addini da al'adu na Iran da suka shirya da zummar wayar da kawunan mutane muhimmancinnkur'ani .Kuma za a samu halartar masana da kwararru daga kasashe daban daban na duniya.
417934