Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga jaridar kasar Bahrain ta Alwaqt cewa; Za a gudanar da wani zaman taro a birnin False na kasar Italia dangane da tarihi da sirar manzon Allah SAW, domin yin nazari kan darussan da ke cikin tarihinsa da kuma yadda ya kamata a fassara addini da abin da ya aikata ko ya umurci a aikata a matsayin ma'aunin gane hakikanin addinin musulunci da koyarwarsa. Bayanin ya ci gaba da cewa za a gudanar da taron ne a cikin shekara mai zuwa, amma yanzu haka an fara gudanar da dukkanin shirye-shiryen da suka kamata, kuma taron zai samu hamalrtar masana musulmi da wadanda ba musulmi ba, domin yin nazari dangane da sirar manzon Allah SAW.
435523