Kamfanin dillancin labaran Ikna ya habarta cewa; An gudanar da bangare na biyu na karshen harda da karatun kur'ani a gasar karatu da hardar kur'ani ta kasa da kasa da aka gudanar a birnin Tehran tsakanin makarantan Iran da kuma na kasar Senegal. Bayanin ya ci gaba da cewa dukkanin bangarorin biyu sun kara da juna a yayin gudanar da gasar, inda daga karshe suka samu kyaututtukan da aka ware ga wadanda suka kai ga mataki na ukun karshe da na biyun karshe a gasar.
438153