Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga bangaren yada labaransa na kudancin Asia cewa; Wani kwamitin malaman jami'a da gwamnatin Indonesia ta kafa ya kirayi dukkanin kasashen musulmi da su yi aiki kafada da kafada. Daga cikin muhimman abubuwan da taron ke yin dubin a kansu har da daukar matakai na mayar da martani a ilmance dangane da yadda wasu masana a jami'oin kasashen turai suke kokarin gurbata manufar addinin musulunci a cikin nahiyar turai, wanda hakan na bukatar masana musulmi musamman ma dai malaman jami'oi su mayar da hankali kansa domin kare addinin musulunci daga zagon kasa.
443071