Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga shafin internet na nasij cewa; Wakilan kasashen larabawa a kungiyar hadin kan kasashen larabawa za su gudanar da zamansu a birnin Alkahira na kasar Masar dangane da batutuwa da suka shafi a halin da ake ciki a birnin Qods. Daga cikin muhimman abubuwan da za su tattauna akwai ci gaba da rushe gidajen palastinawa da Isra'ila ke yi a yankun gabacin birnin Qods.
445282