Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga jaridar tajwid ta kasar Morocco cewa; Za a gudanar da gasar karatun kur'ani ta kasa baki daya a kasar Morocco, wadda za a gudanar a masallacin maulay Yusuf a garin Wujdah da ke kasar ta Morocco a cikin watan Radan mai kamawa. Bayanin ya ci gaba da cewa wanna daya ne daga cikin irin shirye shiryen da ake gudanarwa a cikin watan azumin Ramadan. Yanzu haka makaranta da mahardata na ta yin shiri domin shiga cikin wannan gasar kur'ani ta kasa baki daya.
445220