Kamfanin dillancin labaran Iqna ya nakalto daga jaridar Alkhalij cewa; A yau za a bude wata cibiyar addini da aka sa ma suna cibiyar Zaid, wadda sarkin Hadaddiyar daular larabawa Sheikh Zaid ya dauki nauyin ginawa a kasar. Bayanin ya ci gaba da cewa wannan cibiya za ta gagarumar rawa wajen taimaka ma musulmi tare da bayar da agaji ga mabukata. Daga cikin wadanda za su halarci taron bude wannan cbiya a a yau a manyan jami'an gwamnatin kasar Ethiopia, da kuma shugabannin musulmin kasar gami da limamai. A wajen taron bude cibiyar za a gudanar da jawabai kan muhimmancin budeta da kuma ayyukanta.
463487