Kamfanin dillancin labaran Iqna ya nakalto bangaren yada labaransa na birnin New Dlhi cewa; Reshen Jami'ar Mustafa da ke birnin Qom a Jamhuriyar Musulunci ta Iran ya bude wata cibiyar kula da harkokin kur'ani mai tsarki a kasar India. Bayanin ya ci gaba da cewa wannan cibiya za ta ci gaba da gudanar da ayyukan karfafa sauran cibiyoyin kur'ani na kasar da ma sauran cibiyoyin Musulunci. 465843