Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a Iran Ikna daga yankin Balkan bayan ta nakalto daga jaridar Alrayi ta kasar Koweiti ta watsa rahoton cewa; Zikaj a lokacin ganawarsa da mai kula da harkokin mata a a yankin Rauda a koweiti ya bayyana cewa: a zama da tattaunawa day a yi da mata musulmi mata na kasar Labanon ya ga yadda mata suke taka muhimmiyar rawa ba gajiyawa wajen yadawa da buga kur'ani a kokarin sun wadatar da mabuka wannan littafi mai tsarki mai girma. Ya kuma yi kira ga sauran mata musulmi da hukumomi da mu'assisoshi gami da kungiyoyi da su yi koyi da matan kasar Labanon.
470480