Kamfanin dillancin labaran Iqna ya nakalto daga shafin internet na islam inline cewa; An kammala wani zaman taro da aka gudanar babban birnin kasar Danmark dangane da halin da masallacin Qods ya samu kansa a ciki. Daga cikin wadanda suke samun halartar taron akwai masana kan harkokin tarihi na jami'ar danmak da kuma musulmi mazauna kasar, musamman ma malamai daga cikinsu. 470740