Kamfanin dillancin labaran Iqna ya nakalto; Ma'aikatar kula da harkokin tattalin arziki ta kasar faransa ta sanar cewa za a saka tsarin bayar da bashin banki irin na muslunci a wasu bankunan kasar da nufin jawo hankalin musulmi masu saka hannayen jari.
Bayanin ya ci gaba da cewa wannan wani shiri ne da Faransa ta bullo da shi da nufin jawo hankalin musulmi 'yan kasuwa daga kasashen musulmi daban-daban, wanda hakan zai karfafa tattalin arzikinta, musamman ta fuskar saka hannayen jari a bankunan gwamnati. 471968