Kamfanin dillancin labaran Iqna ya nakalto daga shafin internet na jaridar Al-dastur ta kasar Masar cewa; Za a gudanar da wani zama na kasa da kasa dangane da mahangar addinin muslunci kan sauran addinai da kuma yadda addinin musulunci yake kira zuwa zaman lafiya da fahimtar juna tsakaninsa da saurannaddinai.Bayanin ya ci gaba da cewa wanna taro zai yi dubi kan yadda addinin muslunci yake yin kira zuwa zaman lafiya, sabanin yadda ake yi ma addinin muslunci mummunan kallo a kasashen turai, musamman ma a Amurka. 474557