Kamfanin dillancin labaran Iqna ya nakalto daga kamfanin dillancin labaran resalehabar cewa; Za a gudanar da zaman taro kan dantaka tsakanin mutane a mahangar addinin musulunci, wanda za a gudanar a kasar Turkiya. Taron zai yi dubi dangane da yadda musulunci ke kallon muhummancin kyautata dangataka tsakanin mutane a dukkanin harkokinsu na rayuwar zamantakewa, tare da girmama juna da kuma girmama ra'ayoyi da fahimta kowane bangare. 479474