Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a Iran Ikna ce bayan ta nakalto daga Institut imem ta watsa rahoton cewa: Abdallah bin Abdul Aziz Almusttpha babban sakataren hadin guiwar kungiyar matasa ta duniya ya bada labarin gudanar da wannan taro da zai yi bincike da nazari kan yadda kur'ani ya nuna mu'ijizarsa ta ilimi da kuma yadda hakan yake a cikin hadisan ma'aikin Allah tsira da amincin Allah ya tabbata a gare shi da kuma alayan gidansa tsarkaka.hatta wadanda ba musulmi ba an gayyace su a gurin wannan taro domin sani irin abubuwan alheriri da na ilimi da ke kumshe a cikin kur'ani da hadisan ma'aikin Allah.
486642