Kamfanin dillancin labaran Iqna ya nakalto daga shafin internet ummid cewa; An fitar da wasu rubutaccin wakoki na yabon manzon Allah (SAW) a birnin Bopil na kasar India, domin karanta su a wani taro da za a gudanar a bababr jami'ar birnin. Bayanin ya ci gaba da cewa mawakan kasar India gami da malaman jami'a da dama ne za su halarci gabatar da wakokin na yabon manzon Allah da za a gudanar a babban dakin taruka na jami'ar saifiya da ke birnin. 488819