IQNA

Suriya Ta Yi Allah Wadai Da Kaita Hurumin Masallacin Kudus Da HKI Ta Yi

18:00 - March 07, 2010
Lambar Labari: 1895174
Bangaren siyasa da zamantakewa:ma'aikatar harkokin kasar suriya ta yi Allah wadai da kaita hurumin masallacin Aksa da HKI ta ke yi .
Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a Iran ikna bayan ta nakalto daga majiyar labarai ta gwamnatin kasar Suriya Sana ta watsa rahoton cewa; ma'aikatar harkokin wajen kasar ta Suriya ta yi Allah wadai da yadda haramtacciyar ksar isra'ila ke kai ta hurumin masallacin Kudus a ci gaba da mamaye yankunan Palasdinawa da kuma danne su da wuce gonad a iri da take yi a kai akai har ila yau kuma ta bukaci sauran kasashen musulmi da su dauki matakin kawo karshen wannan mummunan aiki na haramtacciyar kasar Isra'ila da yadda ta ke take dokokin kasa da kasa a kullum.

548626
captcha