IQNA

An Yi Bayani Kan Falalar Ta'akul A Cikin Kur'ani Da Hadisai

15:38 - April 01, 2010
Lambar Labari: 1901265
Bangaren kasa da kasa; Aldaib Walid Al'arusi malamin a mu'assisar koyar da harshen larabci ta kasa da kasa da ke birnin Paris fadar mulkin kasar Faransa a cikin wani jawabi day a gabatar a taron kasa da kasa kan Musulunci da ilimin day a shafi kwalluwa ya yai bayani kan falalar yin tunani da nazari a cikin Kur'ani da hadisan ma'aikin Allah (SWA).
Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar Musulunci ta Iran bayan ta nakalto daga majiyar gwamnatin kasar Koweiti Kuna ta watsa rahoton cewa; Aldaib Walid Al'arusi malamin a mu'assisar koyar da harshen larabci ta kasa da kasa da ke birnin Paris fadar mulkin kasar Faransa a cikin wani jawabi day a gabatar a taron kasa da kasa kan Musulunci da ilimin day a shafi kwalluwa ya yai bayani kan falalar yin tunani da nazari a cikin Kur'ani da hadisan ma'aikin Allah (SWA). Ya kara da cewa wannan na nuni da matsayi da daukakar addinin Musulunci da yadda ke fifita neman ilimi da nazari da kuma bincike.


556137
captcha