Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga kamfanin dillancin labaran WAM an bayyana cewa; za a fara gudanar da wani zaman tattaunawa da bahasi tsakanin manyan addinai na duniya a birnin Sharjah, na haddadiyar daular larabawa da nufin samar da fahimtar juna tsakaninsu mai dorewa. Bayanin ya ci gaba da cewa wannan na daya daga cikin muhimman lamurra da suke da muhimmanci musulmi su mayar da hanakali kansu, ta yadda za a kawo karshe rashin fahimtar juna tsakanin mabiya addinai.558348