IQNA

Wasu Mutane Da Ba A Sani Ba Sun Wulakanta Kur'ani A Yeman

20:42 - April 11, 2010
Lambar Labari: 1905568
Bangaren kasa da kasa; Wani gungu wasu ashararn mutane da ba a san ko su wane ne ba sun sake wulakanta kur'ani mai tsarki a kasar Yeman, lamarin da ya jawo matsanancin fushin al'ummar kasar.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin yanar gizo na kamfanin dillancin labaran marab cewa, Wani gungu wasu ashararn mutane da ba a san ko su wane ne ba sun sake wulakanta kur'ani mai tsarki a kasar Yeman, lamarin da ya jawo matsanancin fushin al'ummar kasar. Bayanin ya ci gaba da cewa dubban mutane sun fito a kan manyan titunan birnin Mahrud na kasar domin nuna rashin amincewarsu da wannan mummunan aiki. A nasu bangaren malaman addini sun gudanar da wani zaman gaggawa domin dauakr matakan da suka dace. 560143
captcha