Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani rahoto da ya nakalto daga wani shafin internet na Musulunci a nahiyar Asia an bayyana cewa, an gudanar da wani zaman taro na kwamitocin da aka kafa domin gudanar da ayyuka na isar da sakon addinin Musulunci a kasashen Sri Lanka da India. Bayanin ya ci gaba da cewa kwamitocin suna gudanar da ayyuka na isar da sakon addinin Musulunci tare da wayarwa wadanda ba musulmi ba kai dangane da sakon da addinin Musulunci yake dauke da shi ga dukkanin 'yan adam.560266