Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin kafar yada labarai na mega cewa, Ana shirin gudanar da wani zaman taro kan harkokin saka hannayen jari a mahangar addinin musulunci a kasar Bahrain, tare da yadda musulunci ya amince a karbi bashi. Bayanin ya ci gaba da cewa, taron za a gudanar da shi ne a mtsayi na kasa da kasa, kuma zai mayar da hankali ne dangane da yadda ya kamata musulmi su karfafa junansu wajen saka hannaayenjari domin samun ci gaban harkokin tattalin arzikin kasashen musulmi. 560698