Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga jaridar kasar Kuwait ta Al-ra'ayi an bayyana cewa, wasu daga cikin kungiyoyin yahudawan sahyuniya na yin amfani da ayoyin kur'ani mai tsarki wajen kafa hujjar cewa birnin Qods mallakin yahudawa ne a tsawon tarihin duniya.Bayanin ya kara da cewa babbar manufar wannan aiki ita ce kara birkita tunanin masu kallon lamarin da hakikanin surarsa ta zaluncin yahudawa a tsakanin al'ummomin musulmi da sauran al'ummomin duniya. 562518