Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, Ministan ma'aikatar kula da harkokin addinin muslunci a kasar Qatar ya sanar da kafa wani sabon kwamitin shirya gasar karatun kur'ani mai tsarki a kasar. Bayanin ya ci gaba da cewa Ahmad Abdullah Al-marwi wanda ya taka rawa a fuskokin yada addini a kasar Qatar kuma yake rike da ma'aikatar kula da harkokin addinin a kasar, shi ne ya shiga gaba wajen ganin an sake gudanar da gyara ta yadda harkar kasar kur'ani za ta kara bunkasa a kasar ta Qatar.564434