Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar musulunci ta Iran Ikna bayan ta nakalto daga jaridar kasar Bahrain Alwasat ta watsa rahoton cewa: a ranar bakwai ga watan Ordebehesht ne na shekara ta dubu daya da dari uku da tamanin da tara reshe na biyar na kotun kafircewa a kasar Bahrain ta yankewa wani dan kasar Bahrain danshekaru goma sha tara a duniya hukumcin zama a gidan yari na tsawon shekara daya a gidan yari. Alkali Hamd bin Suleiman Al Khalifa shugaban wannan kotu zai bayyana matsayinsa na karshe kan wannan hukunci da aka zartar.
570292