Bangaren kasa da kasa;wasu daga cikin wakilan majalisa a Koweiti sun bada shawarar ayar doka ta kafa mu'assisar da za ta bawa jama'a damar wallafawa da yada kur'anai da hadisan ma'aikin Allah tsira da amincin Allah ya tabbata a gare shi da alayan gidansa da sauran littafai da suka shafi ilmomin kur'ani mai girma.
Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar Musulunci ta Iran Ikna bayan ta nakalto daga majiyar jaridar Koweiti Alkabas ta watsa rahoton cewa; wasu daga cikin wakilan majalisa a Koweiti sun bada shawarar ayar doka ta kafa mu'assisar da za ta bawa jama'a damar wallafawa da yada kur'anai da hadisan ma'aikin Allah tsira da amincin Allah ya tabbata a gare shi da alayan gidansa da sauran littafai da suka shafi ilmomin kur'ani mai girma. Muhammad Haif da Salihu Almala,Abdallah Alromi,da Abdallarahman Alaijri ne suka gabatar da wannan shawara.
574975