Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar Musulunci ta Iran Ikna bayan ta nakalto daga majiyar IslamRF ta watsa rahoton cewa; A birnin Gorozni fadar mulkin kasar CCnistan ne komitin musulmin wannan kasa a ranar ashirin da daya ga watan Ordebehesht suka gudanar da taron kasa da kasa karo na uku mai taken Musulunci addinin sulhu. A wajen wannan taro an gayyaci masana musulmi da malamai da malaman jami'a daga kasashen Rasha,Suriya,Jodan,Libya,Marokko,Senegal,Oroguie,Koweiti,Baljuim,Britaniya, Spain,Ostriya da kuma wasu kasashe a ke mamba a cikin kungiyar yan ba ruwanmu.
578322