IQNA

An Soki Rashin Kasancewar Sheikhul Azhar A Zaman Binciken Kuran Da Aka Yi Kan Buga kur'ani

13:38 - May 15, 2010
Lambar Labari: 1922985
Bangaren kasa da kasa; mambobin komitin harkokin addini a majalisar dokokin Masar sun soki Ahmad Aldayib Sheikhul Azahar da Ahmad Nazif firaministan kasar ta Masar kan yadda ba su halarci zaman komitin addini day a yi kan binciken sanin dalilain yin kura-kurai wajen buga Kur'ani mai Girma da kuma bincike kan wadannan kura kurai.




Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a nan Jamhuriyar Musulunci ta Iran Ikna bayan ta nakalto daga jaridar kasar masar ta almisriyun ta watsa rahoton cewa; mambobin komitin harkokin addini a majalisar dokokin Masar sun soki Ahmad Aldayib Sheikhul Azahar da Ahmad Nazif firaministan kasar ta Masar kan yadda ba su halarci zaman komitin addini day a yi kan binciken sanin dalilain yin kura-kurai wajen buga Kur'ani mai Girma da kuma bincike kan wadannan kura kurai. Masu sukan Sheikhul Azahar suna gani bai dace ba a ce bai halarci wajen wannna taro ba ganin yadda wannan zama ked a muhimmanci ga jami'ar da ku ya shafi musulmi na duniya ba wai kawai na kasar Masar ba.

579064
captcha