Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a nan Jamhuriyar Musulunci ta Iran Ikna bayan ta nakalto daga beyazgazete ta watsa rahoton cewa; ma'aikatar da ke kula da harkokin da suka shafi addini a wannan kasa ta Turkiya ta bayyana a kowace shekara kimanin mutane dubu biyu da dari biyar ne a fadin kasar ke samun shadar da ke nuni da cewa sun yi hardar Kur'ani mai girma. Akram Kalash tsohon wakilin ma'aikatar harkokin addini a kasar Turkiya DIB a kasar Saudiya kuma mataikamin shugaban komitin koli na DIB dangane da wannan labari ya bayyana cewa;na kowace shekara kimanin mutane dubu dari biy da saba'in n eke zuwa makarantun hardar Kur'ani a masallatai a fadin kasar da ya hada ,mata da maza.
584528