Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar Musulunci ta Iran Iran Ikna bayan ta nakalto daga Saphinews ta watsa rahoton cewa; a kasar Faransa an gudanar da taro kan bangaren so da kauna a Musulunci da cibiyar Musulunci ta Stains da ke arewacin birnin Paris babban birnin kasar Faransa a ranar asabar sha biyar ga watan khurdad shekara ta dubu daya da dari uku da tamanin da tara hijira shamsiya. Akwai malaman jami'o'I da dama da suka gabatar da jawabai masu gamsarwa kan hakikanin so da kauna a Musulunci.
591614