IQNA

Taro Kan Islam Addinin Yafewa A Kasar Pilifine

17:17 - June 07, 2010
Lambar Labari: 1935743
Bangaren kasa da kasa:taro kan Musulunci addini ne na sulhu da aka fara a ranar asabar sha biyar ga watan Khurdad na wannan shekara ta dubu daya da dari uku da tamanin da tara hijira shamsiya a garin Manil babban birnin kasar Pilifines.



Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar Musulunci ta Iran Ikna bayan ta nakalto daga majiyar watsa labarai ta Manilla Bulletin ta watsa rahoton cewa; taro kan Musulunci addini ne na sulhu da aka fara a ranar asabar sha biyar ga watan Khurdad na wannan shekara ta dubu daya da dari uku da tamanin da tara hijira shamsiya a garin Manil babban birnin kasar Pilifines.Wannan taro kungiyar da ke kula da harkokin addini a wannan kasa ce ta shirya da zummar fadakar da hankulan jama'a kan muhimmancin zaman lafiyar da kuma yadda addinin Musulunci ke sahun gaba a tsakanin sauran addinai a duniya wajen hadin kai da zaman lafiya.


592274
captcha