Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar Musulunci ta Iran Ikna bayan ta nakalto daga majiyar watsa labarai ta ICCUK ta watsa rahoton cewa; taron kasa da kasa karo na sha takwas na karatun kur'ani a kasar Masar ga matasa yan kasa da shekaru ashirin da biyar da za a fara daga sha bakwai zuwa ashirin da biyar ga watan Ramadan a birnin Alkahira fadar mulkin Masar. Wannan gasar karatun kur'ani mai girma ma'aikatar da ke kula da harkokin addini a wannan kasa ta masar ta shirya domin karfafawa matasa karfin guiwa wajen harda da karatun kur'ani mai girma.
592192