Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na jaridar Alrayi ta kasar Kuwait cewa, dan majalisar dokokin kasar kuma wakilin mabiya mazhabar shi'a na kasar a majalisa sayyid walid tabatabai ya gabatar da shawara ga majalisar dokokin kasar Kuwait dangane da samara da bangarorin kula da harkokin al'dun musulunci a dukkanin cibiyoyin ilimi na kasar. Ya ce ya gabatar da wannan shawara ne domin ganin irin tasirin da al'adu suke da shi a cikin zamantakewar jama'a, kuma kula da su zai taimaka matuka wajen yi matasa birki tare da dora su kan sahihin tafarki na musulunci, maimakon kwafar dabi'un turai.597143