IQNA

Malaman Azhar Sun Maida Martani Kan Limancin Mace A Salla A Britaniya

11:15 - June 16, 2010
Lambar Labari: 1940914
Bangaren kasa da kasa; wani adadi na malamai a jami'ar Azhar sun maida martani kan yadda wata mata ta jagoranci masallata sallar juma'a a cibiyar al'adu ta Musulunci a garin Aksford na kasar Britaniya da cewa wannan limamanci ya sabawa tushen Musulunci.
Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar Musulunci ta Iran ikna bayan ta nakalto daga jaridar kasar saudiya ta Alwatan ta watsa rahoton cewa; wani adadi na malamai a jami'ar Azhar sun maida martani kan yadda wata mata ta jagoranci masallata sallar juma'a a cibiyar al'adu ta Musulunci a garin Aksford na kasar Britaniya da cewa wannan limamanci ya sabawa tushen Musulunci. Muhammad Abu Laila malami a jami'ar Azhar y ace limamancin salla da malama Ahil Rida ta jagoranta ya sabawa tushen addini mace ta jagoranci maza sallar jama'a kuma wannan akwai wata manufa kan hakan.





597736
captcha