Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari day a nakalto daga shafin yanar gizo na dunyabulteni an habarta cewa, za a saka littafin aladun musulunci a cikin littafan darasi a kasar Rasha, da zai hada da jami'oi da ma makarantun gaba da sakandare na kasar. Bayanin ya ci gaba da cewa littafin wanda malaman addinin muslunci na kasar gami da malaman jamia suka rubuta, ya samu karbuwa a wajen hukummin ilimi na kasar ta Rasha, kuma tuni aka bayyana shi a cikin littafan da za a rika kyarwa a kasar domin bayar da dama ga dalbai su kara samun masaniya dangane da addinin musulunci. 598058