Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na jazeera net cewa, kungiyar malaman makarantun sakandare na kasar Girka za su gyara wata makaranta a yankin zirin Gaza a garin Jabalia da ke arewacin yankin. Bayanin ya ci gaba da cewa wannan makaranta za a gyara ta ne domin nuna goyon baya ga al'ummar yanki da suke karkashin danniyar yahudawan sahyuniya. 599954