Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani rahoton da ya nakalto daga shafin sadarwa na nun an habarta cewa, za a gudanar da wani zaman taro a birnin Karbala mai alfarma domin bahasin ilmi kan taron maulidin Imam Hussain (AS) da hikimar da ke tattare da hakan. Bayanin ya ci gaba da cewa wannan taro za a shirya shi ne ta hanyar shirye-shiryen da kwamitin shirya taruka na addini a birnin, kuma yanzu haka an fara gudanar da shirin gudanar da taron. 601723