IQNA

Za A Gudanar Da Zaman Taro Na Kasashen Musulmi A Makka

15:47 - June 23, 2010
Lambar Labari: 1945460
Bangaren kasa da kasa; A cikin wata mai zuwa ne kwamitocin bitar alakoki tsakanin kasashen musulmi za su gudanar da zamansu a birnin Makka.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin yanar gizo na sadarwa nasij cewa, A cikin wata mai zuwa ne kwamitocin bitar alakoki tsakanin kasashen musulmi za su gudanar da zamansu a birnin Makka mai alfarma domin tattaunawa. Bayanin ya ci gaba da cewa kwamitocin za su gudanar da taron ne a dadidai lokacin da ake cika shekaru hamsin cur da kafa kwamitocin, wadanda suke tattauna muhimman batutuwa da suka shafi harkokin kasashen musulmi. 602466


captcha