Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, banagaren yada labarai na kasar Lababan ya habarta cewa, an buga tare da fitar da littafin turasuna bugu na dari daya a kasar Labanan, wanda cibiyar nan ta Al bait ta dauki nauyin bugawa kamar yadda ta buga har bugu casa'in da tara. Bayanin ya ci gaba da cewa wannan littafi yana dauke ne da bayanai kan yadda mabiya tafarkin iyalan gidan manzon Allah suke gudanar da ayyukansu na addini, da kuma bayyana matsaya kan lamurra da daman a siyasa. 601932