Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani rahoto da ya nakalto daga shafin sadarwa na saphire news an bayyana cewa za a fara gudanar da wani zaman taro na hadin kai tsakanin mabiya addinin musulunci da kuma mabiya a ddinin kirista a birnin paris fadar mulkin kasar. Bayanin ya ci gaba da cewa taron yana da matukar muhimmanci ga dukkanin bangarorin biyu.
Wannan dai ba shi karo na farko da cibiyar kula da harkokin addinin musulunci a kasar faransa ta shirya gudanar da irin wannan zaman taro ba. Yanzu haka dai ana ci gaba da shirye-shirye fara zaman taron. 608114