IQNA

Gwamnatin Malazia Ta Sha Alwashin Bunkasa Harkar Karatun Kur'ani

14:30 - July 05, 2010
Lambar Labari: 1951555
Bangaren kasa da kasa; Ministan harkokin addinin Musulunci a kasar Malazia ya bayyana cewa gwamnatin kasar ta sha alwashin ganin ta bunkasa harkokin karatu da hardar kur'ani mai tsarki a fadin kasar.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga kamfanin dillancin labaran Bernama a shafinsa na yanar gizo an bayyana cewa, ministan harkokin addinin Musulunci a kasar Malazia ya bayyana cewa gwamnatin kasar ta sha alwashin ganin ta bunkasa harkokin karatu da hardar kur'ani mai tsarki a fadin kasar ta Malazia.

Ahmadsha Abdullah gwamnan lardin sabah ya bayyana cewa, yanzu haka gwamnatinsa na shirin daukar bakuncin wata gasar karatu da hardar kur'ani mai tsarki da za a gudanar a kasar na da wasu 'yan watanni masu zuwa.

609076


captcha