IQNA

Mahardata Kur'ani A Masar Na Rige-Rigen Zuwa Gasar Makka

17:56 - July 22, 2010
Lambar Labari: 1960421
Bangaren kasa da kasa; Mahardata kur'ani mai tsarki na kasar Masar na rige-rigen samun damar zuwa gasar karatun kur'ani mai tsarki da aka baiwa taken Makka, wadda za a gudanar a birnin Iskandariyya na kasar ta Masar.



Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na egynews.net cewa, mahardata kur'ani mai tsarki na kasar Masar na rige-rigen samun damar zuwa gasar karatun kur'ani mai tsarki da aka baiwa taken Makka, wadda za a gudanar a birnin Iskandariyya na kasar.

Bayanin ya ci gaba da cewa za a fara gudanar da gasar ne nan da 'yan kawanaki masu zuwa, inda mahardata kur'ani mai tsarki 47 za su kara da juna, wadanda za su fito daga sassa daban-daban na kasar Masar.

Muhammad Wahdan babban sakataren kwamitin kula da harkokin shirya gasar kur'ani na kasa ya bayyana cewa sun kammala dukkanin shirye-shiryen da suka kamata na gudanar da wannan gasa.

618807



captcha