Cibiyar da kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar Musulunci ta Iran Ikna bayan ta nakalto daga islamenfrance ta watsa rahoton cewa; gidan talbijin na Canal Plus a Faransa a ranekun watan azumi mai albarka na da niyar gabatar da shiri na musamman da malaman addini da masana musulmi za su halarta. A shirin wannan shiri hatta mai gabatar da shirin musulmi ne mai suna Abdul kuma za a fara watsa shirin ne daga ranar laraba ashirin ga watan Murdad a daidai ranar fara zumin watan Ramadana.
619765