IQNA

A Gobe Za A Fara Gudanar Da Gasar Kur'ani Ta Duniya A Malazia

18:58 - July 27, 2010
Lambar Labari: 1962850
Bangaren kasa da kasa; A gobe ne za a fara gudanar kur'ani mai tsarki ta kasa da kasa a birnin Kualalampour na kasar Malazia a karo na hamsin da biyu, da ake farawa a kowace shekara makonni biyu kafin fara azumin watan Ramadan.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a gobe ne za a fara gudanar kur'ani mai tsarki ta kasa da kasa a birnin Kualalampour na kasar Malazia a karo na hamsin da biyu, da ake farawa a kowace shekara makonni biyu kafin fara azumin watan Ramadan mai alfarma.

Bayanin ya ci gaba da cewa makaranta kur'ani gami da mahardata daga sassa daban-daban na duniya musamman ma ksashen musulmi, za su halarci gasar.

Gasar kur'ani ta kasa da kasa da a kae gudanarwa akasar Malazia tan a daya daga cikin gasar kur'ani ta duniya da aka jima ana gudanarwa a kowace shekara.

A cikin shekara ta 1961 ne aka fara gudanar da wannan gasa a kasar Malazia, wadda tsohon fira ministan kasar Tunko Abdulrahman ya kirkiro a cikin shekarar.

621809







captcha