Bangaren kasa da kasa; A gobe idan Allah ya kai mu za a bude wani masallaci da aka baiwa suna masallacin Sayyida Zahra (AS) a garin Saihat da ke gabacin kasar Saudiyya, inda mabiya tafarkin iyalan gidan manzon Allah (SAW) suke fi yawa.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga tashar sadarwa ta Rasid cewa, a gobe idan Allah ya kai mu za a bude wani masallaci da aka baiwa suna masallacin Sayyida Zahra (AS) a garin Saihat da ke gabacin kasar Saudiyya, inda mabiya tafarkin iyalan gidan manzon Allah (SAW) suke fi yawa a kasar.
Rahoton ya ce wannan masallaci mabiya mazhabar shi'a ne suka gina shi da kansu, kujma sun ba shi wannan suna na Sayyid Zahra, domin samun albarkar mai sunan.
621938