IQNA

Palastinawa Sun Bukaci Dakatar Da Ayyukan Mamaya A Yankunansu

17:47 - August 02, 2010
Lambar Labari: 1965968
Bangaren kasa da kasa; Hukumar kwarya-kwaryan cin gishin kai ta palastinawa ta kirayi bangaren haramtacciyar kasar Isra'ila da ta dakatar da ayyukan wuce gona da irin da take aikatawa a cikin yankunan palastinawa da hakan ya hada da gina matsugunnan yahudawa 'yan kaka gida.



Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, wani labari daya nakalto daga kamfanin dillancin labaran saba na palastinu an habarta cewa, hukumar kwarya-kwaryan cin gishin kai ta palastinawa ta kirayi bangaren haramtacciyar kasar Isra'ila da ta dakatar da ayyukan wuce gona da irin da take aikatawa a cikin yankunan palastinawa da hakan ya hada da gina matsugunnan yahudawa 'yan kaka gida a cikin yankunan palastinawanm musamman ma mazauna gabacin birnin Qods.

Ya kara da cewa yanzu haka haramtacciyar kasar Isra'ila ta ci gaba da gudanar da ayyukan mamaya a cikin yankunan palastinawan, duk kuwa da kiraye-kirayen da al'ummomin duniya suke yi mata na ta dakatar da hakan.

624330



captcha