Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wata zantawa da ta hada shi jakadan jamhuriyar Musulunci ta Iran a kasar Malazia Muhammad Mahdi Zahidi ya bayyana cewa, ana bin diddigin dalilan rashin samun iraniyawa a cikin alkalan gasar kur'ani mai tsaki ta kasa da kasa da ake gudanarwa a birnin Kualalampour na kasar Malazia, da za a kammala a cikin mako mai zuwa.
Ya ci gaba da cewa gasar kur'ani ta kasa da kasa da ke gudana a kasar ta Malazia gasa mai matukar muhimmanci a matsayi na kasa da kasa, a kan haka yana da matukar muhimmanci ga Iran ta kasance kan gaba a cikin alkalancin gasar.
Dangane da batun halartar makaranta da mahardata iraniyawa a gasar ya bayyana cewa babu laifi sun yi rawar gani, kuma za su ci gaba da yin dubi kan dukkanin bangarorin halartar makarantan da kuma alkalan gasa.
625649